Sie sind auf Seite 1von 11

KWALEJIN ILIMI TA TARAYYA DA KE KATSINA

(HAƊIN GWUIWA DA JAMI'AR BAYERO KANO)

TSANGAYAR NAZARIN HARSUNA

SASHEN NAZARIN HARSHEN HAUSA

LAMBAR KWAS: HAU 1206

JINGA

DAGA

‘YAN RUKUNI NA BIYU (2)

SUNA LAMBA

ABDULRASHID ABBA FKT/22/HAU/00120

FARIDA SANI FKT/22/HAU/00022

HAMZA IBRAHIM FKT/22/ISL/00159

SA'ADATU NURA BADARU FKT/22/HAU/00194

AMINA BALA HASSAN FKT/22/ISL/00127

TAMBAYA

1a. Su wane ne maguzawa?

1b. Wace irin al'ada ce ta bahaushe ake kira al'adar maguzanci?

1c. Miye bambancin al'adun Hausawa maguzawa da na hausawan yanzu. Dukkan bayanan da za
a yi dole ne a kawo kyawawan misalai da hujjoji.
GABATARWA
Maguzawa wata rayuwa ce wadda Bahaushe ya samu kansa a ciki gabanin karɓar kowane irin
addini. Ita wannan rayuwar ana iya cewa daɗaɗɗa ce tun daga iyaye da kakanni. Malamai sun
tofa albarkacin bakinsu a kan ma'anar maguzawa kamar haka.

Kango A U (2008) ya ce maguzawa rayuwa ce wadda Bahaushe (Bamaguje) ya samu kansa ko


kuma ya tashi a cikinta ba tare da damuwa ko samun wata takura ko hani dangane da irin abin
da yake gudanarwa na rayuwarsa ba wato kamar yadda addini kan shimfiɗa dokoki ga mabiya.

Gambo (2008) cewa ya yi maguzawa ‘yantacciyar rayuwa ce ga Bahaushe (Bamaguje) ta yin


annashuwa kawai. Don haka dai ko ya yane.

Maguzawa yana nufin rayuwar da Bahaushe (wato Bamaguje) yake gudanarwa bisa san rai
nishaɗi da shagulgulan more rayuwa na zaman duniya.

A nawa ra'ayin, kalmar maguzawa na nufin rashin addini. Maguzawa mutane ne da ba su bautar
Ubangiji. A ƙasar Hausa duk mutane da ba su karɓi addinin musulunci ba ana kiransu da wannan
suna na maguzawa,wato masu bin addinin gargajiya.

A ƙasar Hausa, duk Hausawa da ba su karɓi musulunci ba ana kiransu da wannan suna kamar
yadda ake gani a wasu sassan Kano, Jigawa, Katsina da Zamfara.

SU WANE NE MAGUZAWA?
Kamar dai yadda muka sani kalmar maguzawa kalma ce da ta ci karo da ra'ayoyin masana da
manazarta da dama dangane da ƙoƙarin gano asalinta. Ko wane masani da manazarci da irin
kallon da ya yi mata. Duk da yake masana da dama sun yi tarayya kan ra'ayi ɗaya kamar haka.

Kruisius (1915) cewa ya yi “wasu suna da ra'ayin cewa kalma Bamaguje na nufin jinsin na miji na
maguzawa. Ta samu ne a lokacin da fulɓe da laɓe suka karbi sallah, wato suka zama musulmai
ɗan uwansu mai suna Bama ya ƙi yin sallar ya ɗauki ɗabi'ar rabuwa da su a duk lokacin da za su
yi sallah. Tun daga lokacin Bama ya guje wa masu sallah ko ya guji sallar.

Ta haka ne da tafiya tayi tafiya aka haɗe kalmomin guda biyu “Bama” da guje (Bama+guje) aka
sami Bamaguje. Daga nan aka ci gaba da kiran duk marar sallah Bamaguje jam'in mutanen da
suka ƙi yin sallah ‘yan uwan Bama su ake kira maguzawa.
Bargery (1934) yana da ma kusanci da wannan ra'ayin da ke nuna an samo kalmar maguzawa
daga kalmar “majusi” ta harshen larabci. Kamar yadda ya ce kalmar na nufin Arne daga nan ne
aka sami Bamaguje tilo namiji Bamagujiya tilo mace. Maguzanci hanyar rayuwar maguzawa.

Mahdi Adamu (1980) shima ya yarda da wannan ra'ayi mai nuna kalmar ta maguzawa ta samu
ne daga kalmar larabci. “majusi” mai nufin “Arne” ko “Arniya”. Ya ƙara da cewa wata ƙila
Hausawa musulmai sun fara amfani da kalmar ne bayan Addinin Musulunci ya fara yaɗuwa a
ƙasar Hausa a wajajen farkon ƙarni na sha tara (19) wato sunan da aka laƙaba wa Hausawa da
ba su karɓi musulunci ba.

Kamar yadda muka ambata da farko game da maguzawa in da muka ce su dai maguzawa ba
wasu mutane ba ne daban illa Hausawa ne tantagarya ba su da wani harshe daya wuce harshen
Hausa tsantsa.

Don haka ke nan an yi maganar maguzawa za'a iya cewa sune Hausawa masu bin addinin
gargajiya kuma su maguzawa sune Hausawa na asali. Kuma waɗanda ba su yarda da munafunci,
da hassada, da ƙarya, da cin amana, da zalunci ko rub da ciki da dukiyar wani ba.

Su maguzawa mutane ne waɗanda ba su da wani addini da suke bi amma kuma ba su yarda da


ɗaya daga cikin abin da aka lissafa a sama ba.

Dan haka su maguzawa mutane ne da basu bin kowane irin addini sai na gargajiya (tsafi). Amma
kuma suna tsare gaskiya da riƙon amana da kuma kula da haƙƙin kowane abokin zama.

Kuma su maguzawa mutane ne ma'abota son nishaɗi a ko da yaushe dan haka da zarar damuna
ta wuce kafin su fara farauta, zakaga sun ci gaba da yaɗuwa da yan uwansu a kasuwanni a inda
za su fara more rayuwarsu ta hanyar shaye-shayen giya da burkutu. A nan ne zaka ga sun taru
maza da mata iyaye tare da shahararrun makaɗansu waɗanda ke ƙara zuga su a lokacin da suke
gudanar da rayuwarsu ta maguzanci.

HAIHUWA LOKACIN MAGUZANCI


Yawanci idan Bamagujiya ta ga tana da ciki ba za ta ƙara haye tafi ko zuwa ɗebo ruwa da
daddare ba don gudun kar iskoki su musanya mata ɗan cikinta da nasu kamar yadda camfinsu
ya ce. Haka kuma idan cikin ya bayyana ba za ta ƙara zuwa kasuwa ba wai dan gudun kar ta
gamu da mayu su zubar mata da ciki daga nan idan cikin ya kai misalin wata huɗu ko biyar sai ta
fara zuwa daji tana yo itace (sharɓe) tana kawowa gida tana ajiyewa dan tanadin wankan jego
idan cikin ya kai misalin wata bakwai sai mai ciki ta fara shan dauri. Maguzawa ba sa zuwa
goyon ciki idan ma har zasu to sai bayan an haihu anyi suna suke tafiya.

Da zaran an ce Bamagujiya ta haihu ba za a nemi wata (ungozoma) dan ta yanke cibiya ba, sai
dai kawai matan gidan su kirawo wata tsohuwar gidan ta zo ta yanke cibiyar ba tare da yin wata
addu'a ba idan an yanke sai a sami ruwan dumin da za a yi wa jariri wanka ita kuma mai jego sai
a saurara in mahaifar ta faɗi a samo mata ruwan ɗumi taje ta wanke jikinta. Daga ran nan mai
haihuwa za ta fara wankan jego har sai bayan wata ukku ko biyar a da can. Haka kuma daga ran
nan ba zata ƙara shan ruwa ba sai dai tasha dauri ko aɗebar mata tafasasshe daga cikin ruwan
wanka. In ya huce ta sha haka zata zauna har sai ta ya da wanka. Banda wannan kuma daga ran
da mace ta haihu ba za ta fito waje ta zauna ba dole sai ta fito kamar ɗan bida a hannunta. Dan
wani camfinsu ya ce in suka fito waje batare da suna rike da wani ƙarfe ba iskokai za su taba su.

A ƙasar Katsina kuwa yawancin maguzawa da suke zaune a kudancin ƙasar babu ruwansu da
taron suna bayan kwana ukku ko bakwai su a wurin su idan mace ta haihu sai dangin uban jinjiri
su kawo kaji biyu ko ukku na ƙauri. Waɗannan kaji idan an yanke su za a tsigi gashin a zuba a
cikin tukunyar dafa ruwan mai jego. Bayan wannan ƙauri babu wani biki da suke yi sai bayan
kwana arba'in. A duk tsawon wannan lokaci ba a yi wa jariri suna ba ko da yake dai an riga anyi
masa aski da askar gargajiya.

Idan an kwana arba'in sai a yi wani biki da suke kiran sa lantarki. A wurin wannan biki mata ne
kurum suke taruwa kuma kowace mace idan zata zo za ta taho da gudunmawar da za ta bai wa
mai jego.

SUNAYEN HAUSAWAN LOKACIN MAGUZANCI

1. Sammako - yaron da aka Haifa da sassafe

2. Ranau - yaron da aka Haifa da rana

3. Nahantsi - yaron da aka haifa da hantsi

4. Dare - yaron da aka Haifa da daddare

5. Nomau - yaron da aka Haifa ana noma

HAIHUWA BAYAN MUSULUNCI

Addinin Musulunci ya yi umarni cewa mustahabbi ne idan an yiwa mutum haihuwa ya yanka
rago ko akuya a ranar da jaririn ya kwana bakwai kuma wajibi ne a yanka wannan dabbar a
hantsi idan an yanka anyi umarni a ci wani daga ciki kuma ayi sadaka da wani abin. Amman lallai
ne a bayar da sadakar musamman ma ga makwabta idan mutum ya san zai yanka wa yaronsa
dabbar suna to anso ya jinkirta yi wa yaron suna har sai ranar yankan watau ran da yaran ya
kwana bakwai. Idan uban ya san ba zai sami abin yankan ba anso ya yi wa yaransa suna da wuri
tun kafin ya kwana bakwai bayan an aske kan jinjiri a ranar suna.

Haka kuma a ranar suna anso a zaɓa wa yaro suna mai kyau. Don neman albarkan suna.
SUNAYEN HAUSAWA BAYAN MUSULUNCI

Bayan zuwan Musulunci sai sunayen hausawa suka ƙara yawa ga dai sunayan bayin Allah kamar
Annabawa da Sahabbai da waliyyai da na matan su da na yaransu ga kuma sunayen Mala'iku da
suke sawa yaransu. Duk waɗannan sunayen suna sa masu ne dan neman albarka.

1. Muhammad

2. Abubakar

3. Usman

4. Aliyu

5. Umar

AUREN MAGUZAWA

Kafin shiga addinin musulunci hausawa ba sa yiwa yaran su mata aure sai sun balaga sun kai
misali shekara goma sha takwas. Samari kuwa anfi yi masu da wuri misali shekara goma sha
takwas ko ma sha bakwai. Wani lokaci akan yi wa yaro auren gata tun daga shekara goma sha
biyar ko sha shida. Idan kuma antashi auren yawancin saurayin da budurwa akan haɗa su,
kaɗan ne za a sami budurwa ta aure bazawari ko kuma saurayi ya fara da bazawara.

NEMAN AUREN SAURAYI DA BUDURWA

Yawanci saurayi da budurwa su suke fara haɗa kansu game da zaman aure. A bisa al'ada samari
da yan mata suna da wuraren da suke yaɗuwa da juna su yi wasa ko su yi hira daga nan ne zasu
shaƙu da juna har su so juna da aure. Wuraren yaɗuwar tasu su ne kamar a dandali wurin da
yawanci yan mata da samari kan haɗu ayi wasa bayan anci abincin dare kafin ayi barci.

Wani lokaci daga kasuwa sai budurwa ta gayyaci saurayin da take so su tafi gidansu tare idan
taje ta kawo masa abinci sa'an nan su kwana tare suna zance. Irin wannan shi ake kira
“tsarance”. Sau da yawa budurwa take kai saurayi gidansu don ta nuna wa iyayenta ta sami
saurayin da take so.

BIKIN SAURAYI DA BUDURWA

Kafin ranar ɗaurin aure ta zo an riga an raba goro an sanar da dangin ango da na amarya da
kuma abokan arziki. A irin wannan shagali har mariƙa akan gayyata. A wajen wasu maguzawan
kamar na kwatarkwashi idan ya rage kwana biyu a ɗaura auren budurwa sai a sa ta lalle a fara
buki. Amma waɗansu maguzawan basa sa yarsu a lalle sai bayan an ɗaura aure.
A ranar aure jama'a da yawa gayyar dangin ango da na amarya za su haɗu a gidan ɗaurin aure
yawancin maguzawa sukan taho tare da matansu idan kuma za su taho za su yiwo guzurin
kayan abinci da tulunan giya. Jama'a za su rabu inuwa-inuwa. Idan an gama sai ayi izini wata
inuwa don a ɗaura aure dattijai su suka jiɓintar ɗaurin auren. Babban gida ko ɗan uwan uban
yarinya shi zai ɗaura aure. Bayan dattijai sun yi ɗan barkwanci a tsakanin su sai ayi izinin ɗaura
aure. Daga nan sai wani tsoho a cikin dattijan ya ce “ Daram na ɗaura auren wane da wance in
ga ɗan abun ka an uwar da zai raba.

Wannan shi ne kusan lafazin da dukkanin maguzawa suke ɗaura aure da shi.

Daga nan sai amarya da ango kowa ya kama wani wuri daban su shiga taɗi da juna kamar haka.

Ango : wo wance

Amarya : wo wane

Ango : gonar mu daga nan ta kai Sakkwato

Amarya : muna iya nome ta

Ango : wo wance

Amarya : wo wane

Ango : gonar mu daga nan ta kai Kano

Amarya : muna iya nome wa.

Sai kuma muyi maganar tsare-tsaren da suke yi a lokacin bikin saurayi da budurwa sune kamar
haka:

1. Tsare-tsaren maguzawa lokacin bikin

2. Masu tsafin uwar gona

3. Masu tsafin bagiro

4. Masu tsafin kurmawa

5. Tsafin maƙera

AUREN BAYAN MUSULUNCI

Addinin musulunci ya halatta yin aure tsakanin mace da namiji.

Bayan wannan kuma musulunci ya wajabta ba da sadaki ga matar da za a aura.


Sadakin kuma ya zamana bai kasa ɗaya bisa huɗu na zinare ba wannan sadaki ana iya biyan kuɗi
a hannu ko kuma a ɗauka bashi. Haka kuma musulunci ya sharɗanta lallai a sami waliyyai kafin
ayi aure.

Aikin waliyyi shi ne ba da aure. Waliyyi zai zama ɗan uwa ne makusanci a wajen gado dangin
uba ko sarki ko kuma kowane namiji baligi daga cikin Musulmai.

Haka kuma sharaɗi ne a cikin addinin musulunci kafin a yi aure lallai a sami shaidu waɗannan
shaidu suna iya zama mutum biyu adalai ko kuma mutane da yawa.

Kuma sharaɗi ne kafin ayi aure a sami lafazi na bayarwa da na karɓa watau waliyyin amarya ya
ce ya bayar Ango ko Wakilinsa ya ce ya karɓa. Idan an cika waɗannan sharuddan to aure ya
tabbata ke nan abisa ƙa’idar addinin musulunci.

Daga wannan lokaci mace ta halatta ga mijin ta.

ADDININ GARGAJIYA NA HAUSAWA

Mafarin addinin gargajiya shi ne bautar gumaka, watau addinin gargajiya ya wanzu ne ta bin
wasu hanyoyi da mutane suka ƙago wa kansu ta bautar waɗansu abubuwa don cimma biyan
buƙatunsu. Littattafan tarihi sun yi bayanin mutanen da suka fara zama a duniya da kuma
addinin su a gargajiya. Ga misali yan kaɗan daga cikinsu dan share fage ga nazarin da muka
dosa.

MASAR

An ce mutanen masar suna daga cikin mutanen da suka fara zama a duniya.

Waɗannan mutane a zamanin da can sun bauta wa gumaka iri-iri manya daga cikin su su ne: Ra
da Osiris.

RA: shi ne gunkin rana wanda suka ɗauka akan shugaban dukkan gumaka. A ƙudirin su ra shi ne
wanda ya halicci komai na duniya.

OSIRIS: kuma shi ne gunkin da yake bi ma Ra a girma shi kuma shi ne yake sa Kogin nill ya malala
cikin daji yadda jama'a za su shuka amfanin gona.

YADDA HAUSAWA KE ADDININ GARGAJIYA

A) TSAFI: yana ɗaya daga cikin hanyoyin bauta a cikin addinin gargajiya na Hausa. Ta hanyar
tsafi maguzawa sukan bauta wa wani aljani wanda yawanci sukan ce yana zaune akan wani
dutse ko a kogon wata bishiya misali. Tsamiya ko kuka.
B) KAN-GIDA: kan-gida wata al'ada ce wadda ta ke hana jinni ko wani sashi na jikin dabbar da ya
ɗauka ita ce kan-gidansu. Waɗansu sukan ɗauke dabbobi kamar biri ko damisa ko kura ko damo
su zama kan-gidan. Waɗansu kuma su ɗauki irin su macizai da ƙadangaru.

C) BAUTAR ISKOKI (BORI): Ɗaya daga cikin hanyoyin addinin gargajiya na Hausawa ita ce “Bori”
watau bautar iskoki. Bori tsohuwar al'ada ce a wurin Hausawa. Sun fara ta tun lokacin da suke
duk maguzawa ne. Hausawa sun ɗauka ban da ma mutane duniya tana cike da wasu ɓoyayyin
halittu masu ɗabi’u a irin ta mutane har saboda haka suke kiransu “mutanen ɓoye”

D) FARAREN ISKOKI: Sarkin makaɗa da ake kiran sa, sarki makaɗa Abdu jikan Abdu. Ga kuma
kirarin sa kamar haka:

Ɗan abamu jikan kabo.

Mai kiɗa na dama da hauni.

Mai gular azurfa da zinari.

Mai tambura na sarkin aljan.

Kowa yai kiɗa a gunka ya koya.

Sarkin makaɗa yana da mahimmanci acikin iskoki.

MUSULUNCI A ƘASAR HAUSA

Ko daya ke musulunci ya daɗe da shigowa ƙasashen Afrika ta yamma duk da haka bai zo
ƙasashen Hausa da wuri ba saboda rashin samun manyan kasuwanni da kuma kyawawan
hanyoyin safara waɗanda suka haɗa wannan sashi da sauran ƙasashen Afrika ta yamma. A
wannan lokaci kuwa fatake suna daga cikin manyan hanyoyin yaɗa addinin musulunci saboda
haka kafin musulunci ya zo ƙasar Hausa sai da aka sami waɗannan manyan hanyoyin ciniki sun
haɗa ƙasar da ƙasashen da suke bakin gaɓar teku. Hanyoyin sune:

1). Sijilmasa (Morocco) Mauritania- taghata Ta odeni- Tambutu- Katsina- Kano

2). Tarabulus (libya) – Air– Katsina– Kano

3). Masar- Fezzan– Kanemi– Borno– Kano– Katsina

4). Masar barfur– waday– Kanemi– Borno– Kano– Katsina.

MUHIMMAN ABUBUWAN DA MUSULUNCI KE KOYARWA


Addinin musulunci addini ne da ya ƙunshi dukkanin fannonin rayuwar ɗan adam. Don haka duk
wanda ya shiga addinin to rayuwarsa gaba ɗaya ta dogara ne a kan koyarwar addinin. Ita kuma
koyarwar ta kunshi muhimman abubuwa guda huɗu kamar haka.

1. Tauhid (kaɗai ta Allah)

2. Ibada

3. Hanyoyin rayuwa da tarbiyya

a) Tsarin rayuwa

b) Tarbiyya

4. Hukunce-hukuncen sharia.

MUTUWA A MAGUZAWA

Kalmar mutuwa an aro ta ne daga larabci tana nufin faduwa, rabuwa ko sharewa.

Idan an ce rayuwar maguzawa tana nufin rayuwar da aka gudanar kafin zuwan musulunci haka
kuma tana nufin rayuwa da babu tsarin shari’a ko wani saukakken addini akan yi ko bari. Don
haka a rayuwar maguzawa idan an yi mutuwa akan yi abubuwa kamar haka:

1. Yi wa gawa kashedi

2. Kushewa

3. Zaman makoki

4. Rawar mutuwa ta kwanaki ukku, da bakwai, da arba'in da ɗari

1. YI WA GAWA KASHEDI: Anan idan ance kashedi ana nufin jan kunne haka nan idan tsoho ya
mutu to sai a kira dukkan ƴaƴansa da jikokinsa su jera su yi layi kowa yazo kusa da gawar yace
to sauran idan kaje an tambaye ka kace ba kai kadai bane, idan an tambaye ka kace duk kowa
ya tafi babu saura haka za'a dinga yi har sai kowa ya faɗi irin wannan kashedin.

2. KUSHEWA: Anan kushewa nufin ramin da ake saka gawa dan haka duk wanda ya mutu za'a
saka shi a kabari, kuma babu wasu ƙaidoji wajen binne gawar.

3. ZAMAN MAKOKI: Wannan yana nufin lokacin da wani ya mutu to yan uwansa kan taru bayan
an binne shi maza kan zauna a kofar gida haka kuma mata kan zauna acikin gida don karɓar
gaisuwa da nuna alhini sannan ba wata addu'a suke yi ba a'a idan an zo cewa ake yi ashe wane
bai daure ba? Ashe wane yafi muruci ruwa? Ashe wane ya iske shekara? Sannu da haƙuri da
sauran kalamai irin waɗannan.
4. RAWAR MUTUWA: Bayan gama zaman makoki na kwana ukku da gudunmuwar kuka to sai
yan uwa da abokan arziki su yi da’ira su dinga waka suna ambaton sunan mamacin haka za'a yi
bayan kwana bakwai da arba'in da kuma kwana ɗari da mutuwar to amma a kwana na ɗarin
bayan yin rawar za'a zo da tulunan giya da baƙin bunsuru bayan kammala rawar za'a dunga
zuba giya a kan kabarin gawar a kuma yanka baƙin bunsuru a zuba jinin a kan kabarin daga nan
kowa zai watse sai babban ɗa ya gaji komai hadda mata da dukiyar mamacin daga nan ba za'a
sake ko maganar gawar ba.

MUTUWA BAYAN ZUWAN MUSULUNCI

Kamar yadda addinin musulunci ya tsara, mutuwa na da tsare-tsare, watau da zarar rai ya fita
akan shafa ruwa don a rufe idanu, daga nan sai a shiga hidimomin jana'iza kamar haka:

1. Wankan gawa

2. Likkafani

3. Sallar gawa

4. Haƙar kabari

5. Zaman makoki

6. Sadakar ukku, bakwai da arba'in

7. Takaba

8. Gado

1. WANKAN GAWA: bayan da mamaci ya cika abu na farko shine ayi masa wanka da ruwa mai
kyau, irin wankan da ake yi na janaba, da ruwan ɗumi asanya bagaruwa da magarya da ruwan
zam-zam bayan gamawa sai batun likkafani.

2. LIKKAFANI: bayan kammala wanka sai maganar saka likkafani watau yiwa gawa sutura inda
akan yi amfani da falle ukku ko bakwai bayan sanya mashi sai a kawo makara a saka mamacin a
ciki tare da zuba mashi turare a jikin likkafani daga nan sai sallar gawa.

3. SALLAR GAWA: Anan bayan zuwan musulunci idan mutum za'a mashi salla amma ba yadda
ake sallar nafila ba, anan za'a ajiye gawa a gaban liman da sauran jama'a ayi masa addu’o’in
neman gafara za ayi kabbara guda bakwai kuma ita sallar daga tsaye ake yinta daga nan sai
aɗauki mamaci a kai shi kushewarsa.

4. HAƘAR KABARI: bayan gama sallar gawa sai a ɗauki mamaci, idan akaje can maƙabarta, ayi
mashi rami, ramin za'ayi shi da faɗi wajan, sannan ayi ƙarami wajan da za'a saka mamacin akan
hannunsa na dama sannan a sako tukane da ɗanyar ƙasa a kawo busashiya a ɗora, daga nan sai
ayi mashi addu'a neman gafara da ikon amsa tambayoyin Mala'iku

5. ZAMAN MAKOKI: bayan dawowa daga kai mamaci makwancinsa sai zaman makoki idan maza
zasu zauna a waje mata a cikin gida don su amsa gaisuwa da ragowar iyalinsa da raɗaɗin
mutuwarsa, wasu kanyi kwana ukku wasu kuwa kwana bakwai da ga nan za'ayi addu’oi kwana
ukku ko kwana bakwai sai kowa ya koma inda yake wato gidansu ko garinsu.

6. ZAMAN TAKABA: bayan mutuwar mamaci idan yana da iyali (matansa na aure) takaba na
nufin matar mamaci zata ƙwauracewa ƙwalliya da saka tufafi mai ɗaukar ido har na wata huɗu
da kwana goma.

7. SADAKAR ARBA’IN: bayan kwana arba'in yan uwa zasu sake yaɗuwa ayiwa mamaci addu'a
kamar yadda ake yi ta kwana ukku ko bakwai.

8. RABON GADO: anan bayan mutuwar mamaci akan tara dukkanin dukiyarsa abiya mashi
bashi, idan ba a binsa sai a tara yaransa maza da mata yara da manya a rabawa kowa rabon
namiji ɗaya a baiwa mata biyu kamar yadda addinin musulunci ya tsara, idan yana da iyaye a
raye to su ma za a basu rabon su. Idan kuma bai haihuba to iyayensa ko yan uwansa idan babu
iyaye. Wannan shine yadda ake bayan mutum ya mutu a lokacin da addini ya shigo.

KAMMALAWA
A wannan aiki, mun gabatar da bayani akan su wane ne maguzawa da al'adun da Bahaushe
yake kira maguzanci da bambancin al'adun Hausawa maguzawa da na hausawan yanzu

MANAZARTA
Muhammad Sani Ibrahim (1982). Dangantakar al’ada da addini tasirin musulunci kan rayuwar
Hausawa. Sashen Harsunan Nigeriya Jami’a Bayero Kano.

Mu’azu Sa'adu Muhammad (2020) Bahaushiyar al’ada. Published (2020) Bayero University press
main library building Bayero University Kano.

Das könnte Ihnen auch gefallen